Wednesday, 14 September 2016

Kogin Jini a Bangladeshi ya mamaye titi (Hotuna)

Kwanaki kadan da wani kogin jini a kasar Rasha ya ta da hankalin jama’a, sai ga shi wani kogin jini ya mamaye Dhaka babban birnin Bengladeshi

A cewar rahoton jaridar The Sun, manyan titunan Dhaka sun cika da ruwan da launinsa ya koma ja zur! Wanda kuma daga baya aka tabbatar da cewa jini ne na gaske.

Even the roads in Dhaka are not spared from the river of blood.

A cewar rahotanni, jinin da ya mayar da kogin ja, daga dubban dabbobin da ka aka yanka ne a bikin Sallar Layya a kasar a ‘yan kwanakin nan, an kuma kiyasta cewa na yanka dabbobi kimanin 100,000. In ji jaridar.

Bangladesh streets covered in river of blood.

An kiyasta kasar Bengladesh na da kimanin Musulmai miliyan 148 da 600,000 a shekara ta 2011, kuma a bikin na sallar Layya da ake gudanarwa sau daya a shekara ana yanka dabbobin da suka hada da Raguna da tumakai da sauransu a kasar.

Dhaka residents wade through river of blood in the Bangladeshi capital.

Sai dai wannan shekarar an gabatar da Sallar Layya ne a tsakiyar damina, a inda ranar Talata 13 ga watan Satumba ruwan sama ya yi ambaliyar ya mamaye lungu da sako na kasar, a inda magundanan ruwa masu jini, suka cukudu ruwan sama na ambaliyar, ya kuma kwarara zuwa titi.

KU KARANTA KUMA: Mai sayar da mushen kaji ga jama’a ya shiga hannu a Kano

Jaridar ta rawaito wata mace mai suna Attish Saha, wacce ta ke zaune a Dhaka na fadawa jaridar Guardian ta Burtaniya cewa, ganin wannan al’amari ya tayar mata da hankali matuka, domin a ruyuwarta ba ta taba ganin irin wannan al’amari ba.

The post Kogin Jini a Bangladeshi ya mamaye titi (Hotuna) appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.



from Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7 http://ift.tt/2cnk281
via IFTTT

No comments:

Post a Comment

LinkWithin

Related Posts Plugin for WordPress, Blogger...